Ga Wata Dama Ta Samu: Gwamnatin Jihar Kano Zata Bada Scholarship Zuwa Kasashen Waje

Assalamu alaikum warahamatullah barkanmu da sake kasancewa daku a wannan shafin namu mai Albarka.

Gwamnatin jihar kano zata bada scholarship zuwa kasashen wajen a daliban da suke matakin First Class.

Wannan yana daga alqawarurrukan da gwamnatin ta ɗauka lokacin yaƙin neman zaɓe.

SHARUƊAN DA AKE BUKATA SUNE:

  • Ya kasance mai nema cikakken ɗan jihar Kano ne
  • Ya kasance ya gama digiri da First Class a jami’ar da take shaidar tantancewa a hukumance.
  • Ya kasance mai ƙoshin lafiya

ABUBUWAN DA AKE BUƘATA SUN HADA DA:

  • Shaidar zama ɗan jihar Kano
  • Takardar haihuwa
  • Shaidar gama makarantar firamare
  • Shaidar kammala jarabawar sakandare (WASC/GCE/SSCE)
  • Shaidar gama digiri mai ɗauke da First Class.
  • Transcript da makamantansu

Za’a kai waɗannan takardu ne sakatariyar tantancewa dake tsohon dakin taro na ofishin sakataren Gwamnatin Kano kan titin Wudil Road.

A kula: KADA A WUCE SATI 2 BAA KAI WADANNAN TAKARDU BA.

Akwai website da mai nema zai shiga ya cike bayanan sa domin cikawa danna Apply now dake kasa

Apply Now

Allah ya bada sa’a

Join Our Whatsapp Group

Related Articles

Back to top button
error: Alert: Content selection is disabled!!